Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Gudanar Da Zabe A Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya


'Yan gudun hijiya a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya
'Yan gudun hijiya a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya

Masu kada kuria sun tafi runfunar zabe a Jamhuriyar Afrika ta tsakiya bayan shekaru uku ana dage zabe.

Jiya Laraba a jamhuriyar Afirka ta tsakiya, 'yan kasar suka je rumfunan zabe, domin kada kuri'a a zaben kasar da aka sha jinkirtawa, wanda mutane da dama suke fatar zai kawo karshen tarzomar da ake yi shekaru uku ana fama da ita a kasar.

Anga dogayen layuka a Bangui babban birnin kasar, kodashike akwai rahotanni ba'a bude wasu rumfunan zabe akan lokaci ba, duk da haka babu rahotannin anyi arangama ko magudi ba.

An tsananta matakan tsaro a zaben shugaban kasa da 'yan majalisar, da aka shiry za'a yi tun farko ranar Lahadi, amma aka dage da kwanaki uku saboda matsaloli jigilar kayan aiki da kuma kimtsawa.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG