Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Neman Diyyar Fiye Da Naira Miliyan 70, A Hannun 'Yan Sanda


Jami'an 'yan sanda sun Najeriya
Jami'an 'yan sanda sun Najeriya

Majalisar wakilan Najeriya ta umarci kwamitin ta mai bin diddigin korafin Jama’a, ya gudanar da bincike dangane da zargin da ake yiwa ‘yan Sanda a Kano na kisan gilla ga wani mutum mai suna Ibrahim Badamasi na kauyen Gundutse dake yankin karamar hukumar Kura. Al’amarin dai ya faru ne a ranar 14 ga watan Nuwambar bara a yayin arangama tsakanin ‘Yan Shi’a da ‘Yan Sanda akan hanyar Kano zuwa Zaria.

Wasu gungun Lauyoyin kare hakkin bil-Adama ne suka rubuta takardan korafin ga Majalisar wakilan ta Najeriya,suna neman a dauki matakin da yakamata akan ‘yan Sanda, da kuma jami’an kiwon lafiyan da ake zargi da hannu wajan mutuwar wanna magidanci da yam utu yabar ‘ya’ya bakwai da mata biyu.

Garba Ibrahim Diso, dan Majalisar, da ra karata takardan korafin ya ce lauyoyi ne suka rubuto zuwa ga kakakin Majalisar tarayya kuma kakakin ya tura ga kwamitin dake kula da korafe korafe.

Baya ga neman diyyar fiye da Naira miliyan saba’in da biyu, lauyoyin na bukatar a hukunta duk masu ruwa a cikin wannan al’amari.

Da wakilin muryar Amurka Mahmud Ibrahim Kwari, ya tuntubi rundunar ‘yan Sandan jihar ta Kano, rundunar tace bata da masaniya akan wanna al’amari.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:18 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG