Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Anyi Taron Kungiyar Gwamnonin Najeriya, Amma Babu Guda Daga Jam'iyyar PDP da Ya Halarci Taron


Ahmed Bola Tinubu daya daga cikin jiga-jigan jam'iyyar APC.
Ahmed Bola Tinubu daya daga cikin jiga-jigan jam'iyyar APC.

Da yake magana kan taron, gwamnan jihar Sokoto Aliyu Magatakarda wamako, yace sun tattauna kan makomarsu bayan sun kammala wa'adi da kuma samarwa jama'a ayyukan yi.

Jiya Jumma'a kungyar gwamnonin Najeriya karkashin jagorncin gwamnan jihar Rivers Chibuke Rotimi Ameach, i ta kammala taronta na bayan bayan nan a Patakwal babban birnin jihar.

Duka gwamnonin dake karkashin jam'iyyar hamayya ta APC su 11 sun halarci taron, amma babu wani takwaran aikinsu daga jam'iyyar PDP ko daya da ya halarci taron.

A cikin batutuwa da gwamnonin suka tattauna harda irin ayyukanda zasu sa gaba bayan sun kammala wa'adin aikinsu da hanyoynda zasu bi domin samarwa jama'a ayyukan yi, da kiwon lafiya da sauransu.

Gwamnan jihar Sokoto Aliyu Magatakarda wamako, wand a yayi magana da wakilin Sashen Hausa Lamido Abubakar yace kungiyar ta kuma duba irin ayyukan canji da jam'iyyar zata saka a gaba da zarar ta kafa gwamnati a tarayya.

Ga karin bayanai.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:31 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG