Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Azumi: Sarkin Musulmi Ya Kira A Yiwa Najeriya Addu'a


 Sarkin Musulmi Muhammadu Saad Abubakar III.
Sarkin Musulmi Muhammadu Saad Abubakar III.

Mai Martaba Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III ya tabbatar da ganin wata kuma ya kira a fara azumi yau a duk fanin kasar

Yayin da yake yin jawabi ga al'ummar Musulmi dake fadin Najeria Sarkin Musulmi ya umurcesu su yi anfani da lokacin azumi su nemi gafara daga Ubangiji Allah su kuma kyautata rayuwarsu a cikin wannan watan mai alfarma mai dimbin arziki. Lokaci ne na samun gafara da albarka.

Musulman Najeriya
Musulman Najeriya

Ya kara da kiran al'umma su yiwa sabuwar gwamnatin da aka zaba addu'a ta musamman saboda ta ci nasara, a samu zaman lafiya da cigaba mai ma'ana. Idan babu zaman lafiya cigaba da kyautata rayuwa zasu yi wuya. Kasar na bukatar cikakken zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya kira a nemi hadin kan duk jama'ar kasar saboda a tafi tare a kuma tsira tare.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:49 0:00
Shiga Kai Tsaye

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:03 0:00

XS
SM
MD
LG