Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ba a Dakatar Da Jigilar Alhazan Borno Ba In Ji Amirul Hajj


Shehun Borno, Muhammad al-Amin ibn Muhammad el-Kanemi, yana hawan Sallar azumi a Maiduguri.
Shehun Borno, Muhammad al-Amin ibn Muhammad el-Kanemi, yana hawan Sallar azumi a Maiduguri.

Amirul Hajj na Borno ya musanta cewa tashin bam a filin jirgin saman Maiduguri ya sanya an dakatar da kwaso alhazan jihar daga Kasa Mai Tsarki

A yayin da ake ci gaba da kokarin ganin an kammala aikin kwashe alhazan Najeriya daga Kasa Mai Tsarki nan da wa'adin 18 ga watan nan na Nuwamba, hukumomin alhazai na jihar Borno sun fito su na karyata jita-jitar cewa an dakatar da aikin kwasar alhazan jihar saboda dalilan tsaro.

A cikin 'yan kwanakin nan rahotani suka yi ta bazuwa a tsakanin alhazan jihar dake Makka a yanzu cewa wani bam ya tashi a filin jirgin saman Maiduguri lokacin da wani jirgi ke sauka da lahazai, kuma a dalilin haka an dakatar da aikin kwasarsu.

A lokacin da yake karyata wannan labarin, Amirul Hajj kuma mataimakin gwamnan Jihar Borno, Alhaji Zanna Umar Mustafa, yace a idonsa jirage na biyu da na uku suka sauka a Maiduguri, kuma a yanzu haka an shafe watani da dama ko harbin bindiga ba a samu a Maiduguri ba, balle kuma tashin bam.

Amirul Hajjin yace babu wata matsalar tsaro da ake fuskanta da zata shafi aikin kwaso alhazan, ya kuma roki jama'a da su guji yada irin wannan jita-jita maras tushe.

Sa'adatu Mohammed Fawu na tafe da cikakken bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:25 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG