Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jamiyar APC Zata Kai Gwamnatin Jihar Bauchi Kotu


APC
APC

Jamiyar APC ta jihar Bauchi ta sha alwashin gurfanar da gwamnatin jihar Bauchi a kotu

Jamiyar APC ta jihar Bauchi ta sha alwashin gurfanar da gwamnatin jihar Bauchi ta PDP a kotu, domin ta kalubalanci hukuncin da Gwamna jihar Bauchi Mallam Isa Yuguda ya dauka na sake nada wasu sabobin shuwagabanin kanana hukumomi, a jihar Bauchi.

Batun zaben kananan hukumomi a jihar Bauchi abu ne dake ciwa yawancin ‘yan jihar tuwo a kwarya, masammam ma ‘yan siyasa.

Gwamnatin jihar Bauchi, da tayi zama da ‘yan siyasar jihar dangane da batun shirya zaben kananan hukumomi a wannan shekara amma daga baya sai ta noke.

Kakakin ‘yan takaran kananan hukumomi na jamiyar APC na jihar Bauchi yace nada kantomomi abun bakin ciki ne, ya kara da cewa wannan na nuni cewa maganan zabe babu kennan.

Alhaji Kabiru Muhammad, mai tallafawa Gwamna jihar Bauchi a fanin siyasa yace Gwamnati, bata nayin abun da ta keso bane bukatun jama’a take aiwatarwa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:21 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG