Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ban Ki-moon Ya Yi Tur da Hari Kan Wani Asibiti dake Yamal


Ban Ki-moon babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya
Ban Ki-moon babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya

Kamar yadda ya faru a Afghanisatan harin da jiragen sama ke kaiwa kan Yamal a karkashin jagoranci Saudiya ya fada akan wani asibitin jin kai

Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon yayi tir da harin saman da ya fada kan asibiti a kasar Yamal, inda yace asibitoci da ma’aikatansu suna da kariya a karkashin dokokin ayyukan jin kai.

Ya kuma bukaci a gudanar da binciken gaggawa don gano inda matsalar take ba tare da son kai ba, wanda abin ya faru ne a arewacin yankin Saana ta Yamal.

Kungiyar jin kai ta Likitocin nan Doctors Without Borders ta fada a jiya Talata cewa harin sama na sojojin da Saudiya ke jagoranta ne ya fadawa asibitin, amma ba a sami mummunar jikkata ba.

Daraktan kungiyar a Yamal din Hassan Boucenine ya kushe wa gamayyar sojojin masu kai hare-haren da jiragen saman yaki. Yace kwanan nan sai da Doctors Without Borders suka baiwa gamayyar sojojin taron dangin taswirar da zata nuna daidai inda asibitin yake.

XS
SM
MD
LG