Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Barack Obama Zai Karbi Bakuncin Taron Kasashen Asia 10


Malaysia ASEAN
Malaysia ASEAN

Shugaban Amurka Barack Obama, zai bukaci karfafa jagorancin kasarsa da rawar da take takawa a yankin Asia na wasu shekaru masu zuwa, muddin ya karbi bakuncin taron kasashen Asia da ke yankin tekun Pacific har su 10 a taron ASEAN da za a yi a Sunnyland ta California.

Ajandar ranar Litinin da Talata ba zata zama a wani tsantsemin aiki a hukumance ba, domin kuwa so ake ayi walwala da raha a lokaci daya kuma shugabannin su tattauna matsalolin da ya kamata su magance a kasashensu na Asia da kawancensu da Amurka.

Ana sa ran shugaba Obama da zai jagoranci taro zai yi abinda ya kamata ya zama wani sharer fagen ci gaba tsakanin kasashen da Amurka don amfanar juna.

Sannan zai share hanyar alakar kasashen da shugabannin baya masu zuwa a nan Amurka da wadancan kasashen na gabashi.

XS
SM
MD
LG