Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buratai: Za A Ladabtar da Sojoji Dake Shiga Siyasa


Sojojin Najeriya
Sojojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta kafa wani kwamiti da zai bincike zargin da ake yiwa wadansu hafsoshin soji da shiga harkokin siyasa a zaben da ya gabata, musamman zaben shugaban kasa, da zabukan da aka gudanar na gwamnoni a jihohin Ekiti da Ondo da Rivers da kuma Akwa Ibom.

Babban hafsan sojojin Najeriya Laftanar Kanar Tukur Baratai , shine ya yi alkawarin kafa wannan kwamiti domin tabbatar da da’a tsakanin sojojin Najeriya. Babban hafsan yace babu shakka an zargi wadansu sojoji da shiga harkokin siyasa dumu dumu, yace idan bincike ya tabbatar da wadansu jami’an sojan suna da laifi, za a ladabtar da su bisa ga abinda doka ta shinfida.

Yace rundunar sojin Najeriya ba zata lamunci rashin da’a ba, kuma tilas ne sojoji su nisanci harkokin siyasa.

Wannan kwamitin da babban hafsan sojojin Najeriyan ya kafa, na karkashin jagorancin majo janar Adeniyi Oyebade, babban hafsa dake rundunar soji ta daya dake Kaduna, yayinda kanar Abdullahi Salihu zai kasance sakatare.

Sanarwar da rundunar sojan ta aikawa manema labarai, ta bukaci dukan ‘yan Najeriya dake da korafe korafe, game da rawar da sojoji suka taka a zabukan da suka gabata a kasar, da su aike da kokensu ko kuma shaidu ga kwamitin da zai yi zama a rundunar soji ta daya dake Kaduna.

Ga cikakken rahoton da wakilinmu a birnin Ikko Babangida Jibril ya aiko.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:46 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG