Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Batun Cibok ne Ya Mamaye Taron Tattalin Arziki


First Lady Michelle Obama's post on Twitter on abducted Nigerian schoolgirls
First Lady Michelle Obama's post on Twitter on abducted Nigerian schoolgirls

Alhamis dinnan, Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya dauki alwashin fito da dalibai sama da 200 da ‘yan bindiga suka sace, yayin da lamarin sace daliban ya mamaye jawabin bude taron da ya kamata ace ya mayar da hankali ne akan nuna albarkar nahiyar Afirka, dangane da zuba jari a kasar da tafi kowace kasa karfin tattalin arziki a nahiyar.

Da yake jawabi a Taron Tattalin Arzikin Duniya da birnin Abuja yake saukar baki, Jonathan ya godewa kasashen ketare a cikin harda Amurka, Britaniya, Faransa da Chana saboda irin gudunmuwar da suka bayar domin gani an ceto wadannan daliban mata, wadanda aka sace su daga makarantarsu ta sakandare ran 14 ga watan Afrilu.

Mai dakin shugaban Amurka Michelle Obama ta nuna nata goyon bayan akan dandalolin sada zumunci, inda ta saka hoto akan Facebook da Twitter, a cikin hoton akwai sakon da ke cewa tana taya iyalen daliban jimami, kuma tana yiwa yaran addu’a.

Tsohuwar Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka, Hillary Clinton itama ta tofa albarkacin bakinta game da wannan lamari wanda ya jawo hankalin duniya.

Larabannan Sojin Amurka tace masu bada shawarwarinta zasu isa Najeriya a kwanaki masu zuwa, domin taimakawa da harkokin sadarwa, shirye-shirye da tattaro bayanai. Britaniya tayi alkawarin samar da hotunan tauraron dan-adam, inda kuma Faransa tace zata samar da jami’an tsaro. China da Kanada sune kasashe na baya-bayannan da suka yi tayin taimakawa Alhamis dinnan.

Litinin dinnan ma wasu ‘yan bindiga sun kai hari a garin Gamburu dake kusa da iyakar Kamaru da inda suka kashe mutane sama da 200.

Wannan lamarin na Gamburu ya nuna irin gazawar jami’an tsaron Najeriya wajen kiyaye rayukan fararen hula a yankin da ke kara ganin tashe-tashen hankula.
XS
SM
MD
LG