Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Birtaniya Na Ci Gaba Da Ganin Matsala Bayan Ficewarta Daga Kungiyar Tarayyar Turai


Matsalar Birtaniya ta kara zafafa a yau Litinin a daidai wannan lokacin da shugabannin Birtaniyar dana tarayyar Turai suke ta kokarin ganin sun shawo kan lamarin mai ban tsoro.

Biyo bayan yadda masu zaben raba gardama a kasar suka zabi fincike kansu daga cikin kungiyar tarayyar Turai, lamarin da aka bayyana a matsayin abinda ya ruda kasar da rabonta da ganin haka tun bayan yakin duniya na biyu.

A kokarin kwantar da hankalin Birtaniyawan game da rudanin, Ministan harkokin kudin kasar yace, tattalin arzikin Birtaniyya fa yana da karfi tun asali, sannan kofofin kasar a bude suke game da harkokin kasuwanci kamar yadda aka saba.

A dukudukun Litinin din nan dai kasuwanin hada-hadar kudi a Turai suna ta tangadi, sai dai ba kamar yadda aka gani a ranar Juma’a ba, lokacin da kasuwar hannayen jarin birnin London ta yi kasa da kaso 8, kafin daga baya ta dan farfado da kaso 3.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG