Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bom a Gombe


Gwamnan jihar Gombe Ibrahim Dankwambo
Gwamnan jihar Gombe Ibrahim Dankwambo

Rahotanni daga garin Gombe sun ce wani bom ya tashi kuma ya rutsa da rayuka

Bom din ya tashi ne a unguwar da ake kira kasuwar mata inda ya rutsa da rayukan mutane uku.

Mutane ishirin sun samu raunuka a fashewar bom din. Wai bom din wasu su uku suka kawoshi cikin keken napep. Kafin shiga unguwar sosai sai sai suka ga a 'yan kalare sun toshe hanya da suke son su bi. A kokarin juyawa da keken bom din ya tashi.

Jihar Gombe tana fuskantar fashewar bamabamai cikin 'yan kwanakin nan. Haka kuma tana fama da rikicin 'yan bangar siyasa yayin da zabe ke kara karaowa.

Ga rahoton Abdulwahab Muhammad.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:10 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG