Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bom Ya Tashi A JIhar Adamawa


Hoto Harin Bam a Masallacin na Kano, Nuwamba 28, 2014.
Hoto Harin Bam a Masallacin na Kano, Nuwamba 28, 2014.

wani bom da aka binne a kusa da bakin hanya,ya fashe a kauyen Lugdira,dake yankin Maiha wanda yayi sanadiyar asarar rai da kuma raunata wasu ,yayin da suke jin dumi a safiyar yau lahadi

Rahotanni daga arewacin jihar Adamawa,na cewa wani bom da aka binne a kusa da bakin hanya,ya fashe a kauyen Lugdira,dake yankin Maiha wanda yayi sanadiyar asarar rai da kuma raunata wasu ,yayin da suke jin dumi a safiyar wannan rana ta lahadi.

Cikin kwanakin nan ne dai dakarun sojojin kasar,dake samun tallafin yan sakai na maharba da yan kato da gora,wato civilian JTF,suka sami nasarar fatattakar mayakan Boko Haram a yankunan Maiha,Mubi,Hong da kuma Gombi,wanda hakan yasa ake tunanin kafin korarsu tana yuwa,mayakan sun daddasa bama-bamai a wasu wurare da suka yi sansani a baya.

Ga rahoton da wakilinmu Ibrahim Abdul’aziz ya aiko mana daga Yala fadar gwamnatin jihar Adamawa.

Harin Bom A JIhar Adamawa-3:08
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG