Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Ebola Ta Sake Bullowa


Ma'aikatan kiwon lafiya na ebola
Ma'aikatan kiwon lafiya na ebola

Yayinda aka yi makonni ba'a samu sabon kamu da ebola ba sai kwatsam gashi cutar ta sake kunno kai

A karon farko cikin wannan shekarar an samu karuwar wadanda suka kamu da cutar ebola a kasashen yammacin Afirka uku inda har yanzu ake fama da cutar.

Hukumar kiwon lafiya ta duniya ko WHO a takaice tace an samu mutane 124 da suka kamu da cutar a karshen makon jiya.

Kasar Saliyo ce take kan gaba inda mutane 80 suka kamu. Sai kasar Guinea inda aka samu 39. A Liberiya kuwa an samu mutane biyar.

A wani sabon rahoto da hukumar kiwon lafiya din ta fitar jiya Laraba tace akwai bukatar a gaggauta a shawo kan sabuwar barkewar kafin damina ta kankama lokacin da shiga kauyuka zai yi wuya.

Tun lokacin da annobar ta barke mutane kusan 22,500 suka kamu da cutar a kasashe uku kuma adadin wadanda suka mutu ya dara 9,000.

Cutar tayi kamar ta tsaya domin an samu makonni da dama babu sabbin kamu.

Dama kwararru a kiwon lafiya sun yiwa yankin yammacin Afirka din kashedi cewa kada su saki jiki domin cutar ka iya dawowa.

Hukumar kiwon lafiya ta duniya tace jana’izar da aka yi a yankin Lola a kasar Guinea watan jiya ba bisa bin ka’idodin da ta tsara ba yayi sababin da mutane 11 suka kamu da cutar.

Wajibi ne a bi ka’idodin binne gawa domin mutane na iya kamuwa da cutar idan itace tayi sanadiyar mutuwar.

Ranar Litinin din nan aka fara gwajin allurar rigakafin cutar a kasar Liberia.

XS
SM
MD
LG