Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Sankarau Ta Hallaka Mutane 7 A Jihar Neja


A kalla mutane bakwai ne jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da mutuwarsu a sakamakon barkewar cutar Sankarau a jihar Nejan Najeriya.

Daraktan kula da lafiyar jama’a a ma’aiktar lafiya ta jihar Neja Dr Muhammad Usman, ya ce cutar ta barke ne a kananan hukumomin Agwara, Kontagora da kuma karamar hukumar Magama, amma ya bayyana cewa kawo yanzu an sami shawo kan lamarin domin an tura jami’an kiwon lafiya.

Da yake hira da wakilin sashen Hausa na muryar Amurka Mustapha Nasiru Batsari, ta wayar tarho, Dr Muhamad, ya bayyana cewa a karamar hukumar Magama ne lamarin ya fi ta’azzara, domin a karamar hukumar ne mutanen bakwai suka rasu.

Shugaban karamar hukumar Magama, Alhaji Muhammad Mamman Auna, ya bayyana cewa shigowar zafi kuma mutane na kwana cikin dakunansu yasa lamarin ya faru duk da shike an aika da ma’aikata domin fadakar da jama’a kan illar kwana a daki cikin zafi, da kuma samar da magunguna domin tallafawa jama’a.

Yawancin wadanda suka rasu kananan yara ne a cewar shugaban karamar hukumar, kuma a ranar Talatan nan ake sa ran ma’aikatar lafiyar jihar zata yiwa manema labarai cikakken bayani akan barkewar wannan cuta a jihar Neja.

Ga cikakken rahoton Mustapha Nasiru Batsari daga Neja.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:29 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG