Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Tasa Keyar Mutane 8 Zuwa Gidan Yari Saboda Cogen Jarabawa


Ma'aikatan kiwon lafiya
Ma'aikatan kiwon lafiya

An yi karin haske akan sunayen mutanen da aka cafke saboda zarginsu da coge a jarabawar daukan ma’aikatan kiwon lafiya.

Hukumomin shara’a a jamhuriyar Nijer sun yi karin haske akan sunayen mutanen da aka cafke saboda zarginsu da coge a jarabawar daukan ma’aikatan kiwon lafiya.

A wani taron manema labarai da ya kira mai gabatar da kara na Gwamnati Maman Tasiu Isa, ne ya tabbatar da haka gabanin tusa keyar mutane 8 zuwa gidan yari kafin a gurfanar da su gaban kuliya.

Yana mai cewa sai da aka bincika takardun sakamako 28,000 aka sami kurakurai dayawa bayan haka mutane dayawa sun kai kara. An samu wasu da basuyi jarabawar ba amma sun samu, an kuma samu wasu da suka yi jarabawar amma basu samu sakamakon kirki ba amma a sauya an basu babbar sakamako saboda haka dole ne a dauki mataki a kasa.

Ya kara da cewa kurakurai da aka samu sun isa a soke jarabawar domin bai kamata ba ace an dauki mutanen da basu cancanta ba a kowane irin aika balema ace kiwon lafiyar mutane.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:22 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG