Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dambarwar Siyasar Majalisar Dokokin Tarayyar Najeriya Abin Kyama ne-Dr. Dukawa


Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.
Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.

Dambarwar siysar da ta dabaibaye Majalisar Dokokin Tarayyar Najeriya a matsayin babban abin takaici, da kyama da kuma ban mamaki. Kasancewa jam’iyar da ta hau karagar mulki ta hanyar zabe, ta nuna a fili cewa, bata so ta kyale ‘yan majalisa su zabi shugabanninsu ta hanyar zabe.

Dr Ahmed Dukawa na jami’ar Bayero Kano, ya bayyana dambarwar siysar da ta dabaibaye Majalisar Dokokin Tarayyar Najeriya a matsayin babban abin takaici, da kyama da kuma ban mamaki. Kasancewa jam’iyar da ta hau karagar mulki ta hanyar zabe, ta nuna a fili cewa, bata so ta kyale ‘yan majalisa su zabi shugabanninsu ta hanyar zabe.

Dr Dukawa ya bayyana cewa, jam’iyar APC ta bayyana karara cewa, so take tayi nadi ba zabe ba, duk da yake tana ikirarin cewa, jam’iya ce mai neman ganin an yi adalcil, wanda bisa ga cewarshi ba daidai bane a tsarin damokaradiya. Yace damokaradiyar cikin gida da ake Magana a kai ta ce, sai dukan ‘ya’yan jam’yar sun amince da dukan wadansu mukamai a yisu ta hanyar zabe, kuma duk wani wanda za a tsayar takara, a yishi ta hanyar zabe, kuma dukan wanda ‘yan majalisa zasu zaba a matsayin shugaba, a yi shi ta hanyar zabe, to a nan ake damokaradiyar cikin gida, amma wannan da suke nuna cewa, wane shine wane, to wannan ba damokaradiya bace, sun nuna cewa nadi ne suke so su yi wanda wannan , tawaya ce a tsarin damokaradiya.

Dangane kuma da ba hammata iska da ‘yan majalisar suka yi, Dr Abati yace, bai kamata su bari a kai ga haka ba, ganin irin yanayin da kasar ke ciki da kuma yanayin da jam’iyarsu ta APC ke ciki, kasancewa mutane suna ganin APC tamkar kishiyar PDP, saboda haka ba a zaci zasu tsaya suna bata lokaci a kan batun raba mukamai ba.

A cikin hirarsu da wakilin Sashen Hausa Mahmud Ibrahim Kwari, Dr Dukawa yace mafita kawai ita ce, APC ta koma tsarin damokaradiya, idan ba haka ba, zata yi ta asarar membobi. Bisa ga cewarshi, abinda kawai ya kamata tayi shine ta amince da duk zabin da ‘yan majalisa suka yi.

Ga cikakkiyar hirar:

Dambarwar Siyasar Majalisar Dokokin Tarayyar Najeriya Abin Kyama ne - Dr. Dukawa - 4'15"
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:15 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG