Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dan Kunar Bakin Wake Ya Kai Hari a Jos Jahar Flato


Hari bom din da aka kai da mota a Jos, Mayu 22, 2014.
Hari bom din da aka kai da mota a Jos, Mayu 22, 2014.

Maharin ya auna 'yan kallon kwallon kafa ne a wani wuri inda aka samar da talabijin domin masu sha'war kallon kwallon kafa.

Jami’an gwamnatin Najerya sun ce wani dan kunar bakin wake ya auna wasu masu kallon kwallon kafa a Jos a daren jiya Asabar, ya halaka akalla mutane biyu.
Nan da nan dai babu wanda ya fito ya dauki alhkain kai harin.

Tagwayen harin bama bamai da aka kai a Jos din ranar talata data shige, sun halaka mutane 130. An aza laifin hare haren kan kungiyar Boko Haram. Kungiyar ta dauki alhakin sace ‘yan mata ‘yan makaranta su fiyeda dari uku, haka kuma ana dorawa kungiyar laifin kashe dubban mutane.

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da gwamnatinsa suna fuskantar fushin ‘yan kasar da kuma sauran duniya domin kasa kubutadda ‘yan matan.

Ga 'yar tattaunawar da Halima Djimrao tayi da wakiliyar Sashen Hausa A Jos Zainab Babaji.
XS
SM
MD
LG