Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dokar Jihar Ekiti Ba Zata Kawar da Rikici Ba - Makiyaya


Kiwon shanu
Kiwon shanu

Wasu kungiyoyin makiyaya na Nigeria sunce sababbin dokokin da gwamnatin daya daga cikin jihohin kasar ta kafa a kwannakin nan ba zasu yi maganin rigingimmun dake yawan barkewa tsakaninsu da manoma ba, abinda ya sha janyo asaran rayukkan mutane da yawa a kasar.

A ranar Litinin da ta gabata ne gwamnan jihar Ekiti dake kudu-maso-yammacin Nigeria, Peter Ayodele Fayose, ya rattaba hannu akan wata dokar da ta takaita kiyon dabbobi akan wasu kebatattun wurare na hukuma, kuma kiyon da rana kawai aka yarda a yi shi, sannan kuma ta haramta wa makiyaya daukar makamai.

Wani kakakin gwamantin ta Ekiti yace fitowa da wannan dokar ta biyo ne bayan barkewar fadace-fadacen da suka faru ne a kwanan nan a tsakanin manoma da makiyaya.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG