Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Donald Trump Ya Zabi Nikki Haley A Matsayin Jakadiyar Amurka A MDD


Nikki Haley
Nikki Haley

Yau Laraba shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump, ya ayyana gwamnar Jahar North Carolina, Nikki Haley a matsayin Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya. Kuma itace mace ta farko da ya nada a majalisar zartaswarsa.

‘Yar shekaru 44, Haley, wacce asalin iyayenta ‘yan kasar Indiniya ne, ta na kan wa’adinta na biyu ne a matsayin gwamnar Jahar ta North Carolina, sai dai ba ta kwarewa kan harkokin difilomasiyya.Ita ce kuma ta farko ta zama da Mr. Trump ya zaba a gwamnatinsa, wacce ba farar fata ba.

A lokacinda yake ayyanata, Trump ya ambato ziyarar aiki data kai kasashen waje da nufin kulla yarjejeniyar cinakkaya a madadin jahar Carolina ta arewa, da kuma shawarwari da kamfanoni na kasashen ketare.

Gwamna Haley dai bata goyi bayan Trump ba, lokacinda ake yakin neman zaben fidda dan takara.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG