Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ebola: Cutar ta Sake Bullowa a Kasar Liberia


Kungiyar mata a Liberia da suke murnar karshen cutar ebola amma sai gashi ta sake dawowa bayan 'yan watanni da aka sanarda duniya cewa kasar ta rabu da ita
Kungiyar mata a Liberia da suke murnar karshen cutar ebola amma sai gashi ta sake dawowa bayan 'yan watanni da aka sanarda duniya cewa kasar ta rabu da ita

A kasar Laberiya kuma, gawar wani matashi dan shekaru 17 da haihuwa ta nuna cewa kwayar cutar nan ta Ebola ce ta kasha shi, bayan wani gwajin da aka yi. Wannan shine karo na farko da aka sami wani da cutar Ebola tun bayan da aka ce kasar ta rabu da cutar ranar 9 ga watan Mayun shekarar nan.

Mataimakin ministan kiwon lafiyar Laberiya Mr. Tolbert Nyenswah, yau Talata ya jaddada cewa kada hankalin jama’a ya tashi. Ya ce an binne matashin bisa ka’idodin da suka kamata a bi kuma jami’an dake bin sawun wadanda matashin yayi mu’amalla dasu sun riga sun fara aiki.

Rahotanni daga kamfanin dillancin labaran AP ya nuna cewa matashin dan shekaru 17 da haihuwa ya rasu ne ranar 24 ga watan nan na Yuni.

Matashin dai ya rasu ne a garin Margibi, wanda yake nesa da inda aka saba ganin wannan cuta, watau dab da iyakokin kasar da Guinea da Saliyo, kasashe biyu da suma su ka ji jiki sosai da cutar Ebola. Mr. Nyenswah yace kwararru na kokarin gano ko matashin ya kama cutar ne a lokacin da yayi tafiya.

Garin Margibi na kusa da tashar saukar jiragen saman Monrovia, tazarar kilomita 50 a kudu da babban birnin kasar.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG