Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Faransa Ta Nemi Hadin Kan Najeriya Da Kamaru Domin Ceto Mutanta Da Ake Garkuwa Da Su


Ministan harkokin kasashen ketare na Kasar Faransa Laurent Fabius
Ministan harkokin kasashen ketare na Kasar Faransa Laurent Fabius
Ministan harkokin kasashen ketare ya gana da jami’an Najeriya da kuma na Kamaru a yunkurin ceto Faransawa takwas da suka hada da mutane bakwai iyalin gida daya da aka yi garkuwa da su wata guda da ya shige.

Laurent Fabius yace an yi garkuwa da wani injiniya kuma dan kasar Faransa a Najeriya cikin watan Disamba.

Fabius ya yi hira da manema labarai bayan tattaunawarsu da shugaban kasar Najeriya Goodluck Jonathan jiya asabar.

Ya bayyana cewa an ga mutanen bakwai ‘yan gida daya a wani hoton bidiyo da aka sa a yanar duniyar gizo ta Yutub a bakin gandun dajin kasar Kamaru dake lardin arewacin kasar wata guda da ya shige. Hukumomi suna kyautata zaton cewa, an sace iyalin ne a Kamaru aka tafi da su Najeriya

Ministan harkokin kasashen ketare na Najeriya Olugbenga Ashiru yace gwamnatin tarayyar Najeriya da dukan hukumomin tsaro suna yin iyaka kokari na ganin an saki mutanen da ake garkuwa da su lami lafiya.

Kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin garkuwa da su. Kungiyar ta shiga kai kare hare a fadin Najeriya a matsayin maida martani da matakin da sojojin Faransa suka dauka a Mali.
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG