Gobarar da tayi sanadiyar mutuwar wani mutum da matarshi mai ciki da kuma ‘ya’yanshi biyar ta tashi ne a wata unguwa da ake kira Alkahira a yankin Arawa dake jihar Gombe.
A cikin hira da Muryar Amurka, wani dan’uwan mamacin ya bayyana cewa, maigidan dake aiki a wani gidan mai, ya dawo gida da yamma ya tarar an dauke wutar lantarki. Bayan sun kwanta da dare aka kawo wuta da misalin karfe goma sha daya na dare sai gobara ta tashi. Ya bayyana cewa, gobarar ta lashe komi a cikin gidan
Karamar yarinyar ta tsira ne lokacin da ta fita tana kwankwasawa makwabta kofa domin neman taimako, yayinda mahaifinta ya shiga inda sauran ‘yan’uwanta suke kwance yayi kokarin fitar dasu ta bayan gida amma hayaki ya turnuke dakin, suka kasa fita dukansu suka gamu da ajalinsu.
Yanzu haka dai yarinyar da ta tsira daga gobarar tana zama da kakarta.
Ga rahoton da wakilin Sashen Hausa Abdulwahab Mohammed ya aiko daga Bauchi.