Wata Hukumar Bincike ta Majalisar Dinkin Duniya ko M-D-D da aka kafa don ta binciki zargin taka hakkokin bil adama da akace anyi a kasar Eritrea tace tana son a kafa wani Kwamitin musamman ko Kotu da zasu saurari irin zarge-zargen da ake yi wa shugabannin Eritrea din, wadanda akace sun fi shekaru ashirin suna taka hakkokin mutanensu yadda suka ga dama.
A cikin rahoton da Hukumar mai wakilai ukku ta bayar,kamar yadda daya daga cikin wakilan, Sheila Keetharuth ta gabatar, an nuna cewa abubuwan da ake zargin shugabannin na Eritrea da aikatawa sun hada da salwantar da mutane, ganawa wasu azaba da kuma kashe-kashen gilla na ganganci a hannun hukuma.
Hukumar Binciken ta MDD dai ta tara bayanan shaida daga wajen ‘yan kasar ta Eritrea su 833 a kasashe 13, ta kuma karbi rubutattun bayanai kamar 160.