Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka tace zata daukaka kara a kan hukuncin kotun tarayya dangane da dokar da zata bada damar dakile ‘yancin bakin haure


In this June 15, 2010 file photo, Arizona Gov. Jan Brewer speaks in Phoenix. With the scrawl of a pen, Brewer awakened a dormant, but politically explosive issue of illegal immigration, sending shock waves across the political spectrum in an election year
In this June 15, 2010 file photo, Arizona Gov. Jan Brewer speaks in Phoenix. With the scrawl of a pen, Brewer awakened a dormant, but politically explosive issue of illegal immigration, sending shock waves across the political spectrum in an election year

Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren.

Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren da basu da takardun izinin shiga Amurka, a dai dai lokacin da dubban mutane ke ci gaba da zanga-zangar nuna rashin amincewa da aiki da dokar da ta fara aiki a Arizona tun daga jiya Alhamis. Lauyoyin dake baiwa Gwamnar jihar Arizona Jan Brewer kariya, sun shigar da daukaka kararsu a babar kotun daukaka kara dake San Francisco, California. Lauyoyin sun kuma bukaci kotun daukaka karar ta gaggauta yanke hukunci.Yayin da ake wannan, ’yan sanda a Phoenix sun kama mutane sama da talatin saboda toshe titunan da ake bi a zanga-zangar da suka shirya a wajen ofishin shugaban ‘yan sanda jiya Alhamis.Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren da basu da takardun izinin shiga Amurka, a dai dai lokacin da dubban mutane ke ci gaba da zanga-zangar nuna rashin amincewa da aiki da dokar da ta fara aiki a Arizona tun daga jiya Alhamis. Lauyoyin dake baiwa Gwamnar jihar Arizona Jan Brewer kariya, sun shigar da daukaka kararsu a babar kotun daukaka kara dake San Francisco, California. Lauyoyin sun kuma bukaci kotun daukaka karar ta gaggauta yanke hukunci.Yayin da ake wannan, ’yan sanda a Phoenix sun kama mutane sama da talatin saboda toshe titunan da ake bi a zanga-zangar da suka shirya a wajen ofishin shugaban ‘yan sanda jiya Alhamis.

XS
SM
MD
LG