Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Jihar Damagaram a Shirye Take Don Taimakon 'Yan Gudun Hijira


Yan Gudun Hijira a Jihar Damagaram
Yan Gudun Hijira a Jihar Damagaram

Ana samun karin 'yan gudun hijira suna shiga jihar Damagaram a kasar Nijar.

Dubban mutane ‘yan gudun hijira na tururuwa zuwa jihar Damagaran a kasar Nijer, a cewar gwamna jihar Damagaran Malam. Kalla Muktari, yace suna samu ‘yan gudun hira da suke shigowa jihar, kumaa shirye suke su taimaka ma duk wadanda ke da bukatar taimako.

Duk dai da cewar wadan da ke shigowar suna zama inda ‘yan uwansu ne kuma har zuwa yanzu babu wani wanda yazo da bukatar neman taimako. Yace gwamnatin shi tashirya don samar da sansanin ‘yan gudun hijira idan bukatar hakan ta samu. Kuma yana kara kira ga al’umar jihar da su cigaba da taimaka ma masu gudun hijirar, kuma su mai da hankali wajen tantance mugu da mutane na kwarai, don kada su kawo matsaloli a cikin jama’a.

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:14 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG