Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Taraba ta dorawa Boko Haram alhakin kisan gilla a Gashaka


Irin barnar da 'yan Boko Haram suka haddasa
Irin barnar da 'yan Boko Haram suka haddasa

Gwamnatin Taraba tace da hannun kungiyar Boko Haram a harin da aka kai kauyukan Gashaka wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da talatin ya kuma raba wasu sama da dubu hudu da muhallansu

Gwamnati jihar Taraba ta ce tana tuhumar kugiyar Boko Haram da kisa harin da ya haddasa asarar rayuka talatin kana ya raba mutane sama da dubu hudu da muhallinsu a kauyuka biyar na karamar hukumar Gashaka da ke jihar Taraba.

Mai baiwa gwamnan jihar Taraba shawara kan harkokin tsaro Kanal Angyo mai ritaya ya yi wannan kalamin da yake bayanin bincike da suka gudanar kan harin da aka kai kauyukan Dorei, Angwai, Mai tsuma na daya da Mai tsuma na biyu.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Taraba Alkali Shaba ya tabbatarwa Muryar Amurka kuma sun kama wani Jauro mai suna Ayuba Ishaku da hanu dumu-dumu wajen yin anfani da gidansa inda aka shirya hari na baya-bayan nan.

Ga karin bayani

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:06 0:00

XS
SM
MD
LG