Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Tarayya Ta Dauki Matakin Shawo Kan Cutar Kwalera a Plato


Wata mace mai fama da cutar kwalara
Wata mace mai fama da cutar kwalara

Ministan lafiya, Farfesa Onyebuchi Chukwu ya bada umurni ga ma’aikatar kiwon lafiya ta kasa ta shiga aiki a jihohin da aka sami barkewar cutar kwalera kwanannan, da ta kashe kimanin mutane 80 a jihohi 7.

Ministan lafiya, Farfesa Onyebuchi Chukwu ya bada umurni ga ma’aikatar kiwon lafiya ta kasa ta shiga aiki a jihohin da aka sami barkewar cutar kwalera kwanannan, da ta kashe kimanin mutane 80 a jihohi 7.

Yayinda aka aika da kungiyoyin zuwa jihohin da suka kamu domin su kare barkewar, ministan yace yanayin da ya kawo barkewar kwalera basu karkashin ayyukan ma’aikatar lafiya ta tarayya, amma na wadannan jihohin da wadansu ma’aikatun gwamnatin tarayya.

Yayinda yake Magana ta bakin jami’in watsa labarai na ma’aikatar Mr Dan Nwomeh, Farfesa Chukwu ya kara da cewa, ko da yake aikin kare kamuwa da cutar basu karkashin ma’aikatar gwamnatin tarayya duk da haka ma’aikatar zata yi iyakar iyawa wajen jinya da ganin cewa ba a sake samun irin wannan matslar bat a wajen yin aiki da jihohin da kuma wadansu ma’aikatun gwamnatin tarayya domin kauda matsalar.

Shi ma da yake bayani a kan matsalar cutar kwalara a garin Ibadan, Dr Oladimeji Olayinka, kodinato na kudu maso yamma, na shugaban kananan asibitoci na kasa, ya bayyana cewa babu wata allurar rigakafi da akayi domin kare cutar kwalera. Yace abu mafi muhimmanci da ake bukata domin kare kamuwa da cuta da kuma yaduwarta shine ruwa mai tsabta. Yace ma’aikatar ta aika da maganin sha na ruwa ga jihohin dake kuduncin kasar, kamar yadda jihohin dake wannan sashen suka sayi wannan magani da yawa a matsayin matakin kare wannan matsala.

Dr Olayinka yace yin amfani da maganin ruwa bisa ka’ida ga marasa lafiya masu fama da kwalera, zai taimaka wajen maida ruwan jikinsu kuma ya taimaki jiki yakin cutar kamin mara lafiyar ya sami magani a asibiti.

Kodinatan sashin, wanda yace ma’aikatar tana binciken dukan ruhotannin cutar kwalera a yankin, yace, raguwar ruwan jiki ne ke kashe mutane, musamman ga yara. Saboda haka yace ana bukatar kula wajen ganin an ba wanda ya kamu da cutar kwalara ruwa domin shine zai ceci ran mutumin.

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG