Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shekau mu Zamuyi Maganin ka


 Dan kungiyar Civilian JTF.
Dan kungiyar Civilian JTF.

Har yanzu Sojoji ke Rike da Garin Bama

Bayan harin da ake kyautata cewa ‘yan Boko Haram ne suka kai garin Bama a jiya, wanda ya dagulawa garin lissafi, wani sabon alamura ne ke kuno kai, na karyata wannan batu na cewa ‘yan kungiyar Boko Haram ne ke rike da garin Bama.

A wani taron manema labarai da kungiyar civilian JTF suka kira yau a garin Maiduguri, sun ce ba gaskiya bane furushi da akeyi cewa ‘yan Boko Haram, sun karbe shugabancin ragamar garin, da kuma barikin sojoji dake cikin garin Bama.

Tun a jiya ne dai aka dinga ganin mutane da dama masamman mata da yara na kwararowa cikin Maiduguri, daga garin Bama sakamakon karan harbe-harbe bidiogogi.

Sai dai kawo yanzu babu wani jawabi daga hukumomin tsaro, game da wannan nasarori da aka samu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG