Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Harin Bam Ya Hallaka Mutane 5 Da Jikkata 11 A Mogadishu


Wani harin bam din da aka kai ta wata mota ya hallaka mutane 5 ya kuma raunata wasu 11 a wajen wani wurin duba ababen hawa da ke daura da Fadar Shugaban Kasa a Mogadishu, babban birnin Somaliya jiya Talata.

Wani mai magana da yawun gwamnatin yankin ya ce harin bam din ya auku ne a harabar babban dandalin kasa. Ya ce uku daga cikin wadanda su ka mutu din sojoji ne.

Kungiyar al-Shabab mai tsattsauran ra'ayin addini ta dau alhakin kai harin. Wannan kungiya mai alaka da al-Qaida, ta kai hare hare da dama a birnin na Mogadishu, ciki har da harin bama-bamai da bindigogi kan otal-otal da wuraren cin abinci da jami'an gwamnati su ka fi zuwa.

Kungiyar ta'adda ta al-Shabab, na daya daga cikin manyan kalubalolin da sabon Shugaban Somaliya Mohammed Abdullahi Mohammed, ya ke fuskanta.

Mayakan na al-Shabab, sun ayyana shi a zaman wanda ya yi ridda, suna masu gargadin 'yan Somalaiya, cewa kar fa su ba shi goyon baya.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG