Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwoza Garin Da Aka Kwato a Hannun Boko Haram, Afirilu 8, 2015

Garin Gwoza na daya daga cikin garuruwan da aka kwato daga hannun 'yan kungiyar Boko Haram a kwana kwanan nan.

Kowace rana nazuwa ne da rahotannin kisan kiyashi, da gano manyan kabarurrukan da aka bizne jama’a da dama a garuruwan da aka kwato a hannun kungiyar ‘yan ta’adda wadanda suka kafa “daular islama” a fadin babban yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Kungiyar Boko Haram ta kai kusan shekaru shidda tana tawaye a Arewa maso gabashin Najeriya kuma ta hallaka dubun dubatar jama’a. An bada rahoton 10,000 a shekarar da ta gabata da kuma raba sama da miliyan 1.5 da muhallan su.

Domin Kari

XS
SM
MD
LG