Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hong Kong Ta Gudanar Da Babban Zaben Ta Na Farko


A Jiya Lahadi ne Hong Kong ta gudanar da babban zabenta na farko tun babbar zanga zangar ‘yan rajin dimokaradiyya a shekara ta 2014, a daidai lokacin da kiraye-kirayen ayyana 'yancin kai da kuma kyamar China ke yaduwa tsakanin matasa masu kada kuri'a.

Masu kada kuri’a dai sun zabi ‘yan Majalisu har 70, a inda masu rajin dimokaradiyya ke fatan su sami akalla sulusi, wato kashi ‘daya cikin uku, na ‘yan Majalisun, domin samun damar dakatar da duk wani yunkurin masu goyon bayan China a kokarinsu na samar da doka.

A wata karamar zanga zanga an bukaci shugaba Leung Chun-ying, wanda China ke marawa baya da yayi murabus, a wajen rumfar da ya kada kuri’a, yayin da wasu kuma ke bayyana kudurunsu na sa ido kan harkokin gwamnatinsa.

Ana dai kyautata tsamanin yau litinin za a fitar da sakamakon zaben.

Hong Kong dai ta zamanto fagen dambarwar siyasa tun zaben ‘yan Majalisar da aka yin a baya bayan nan a shekara ta 2012, wanda yayi sanadiyar fara babbar zanga zangar masu rajin kare dimokaradiya a shekara ta 2014.

XS
SM
MD
LG