Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

EFCC na NemanTsohon Gwamna Jihar Adamawa Murtala Nyako


EFCC
EFCC

Hukumar yake da almundahana wato EFCC tana neman tsohon gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako,

Hukumar yake da almundahana wato EFCC tana neman tsohon gwamnan jihar Adamawa Murtala Nyako, domin amsa tambayoyi game da binciken da hukumar keyi dangane da zarge-zargen da ‘yan majalisar jihar sukayi batun da ya jawo dambarwar tsige gwamna.

Tun farko dai kakakin hukumar Mr. Wilson Ewuzenye, yace suna neman Nyako ne dangane da binciken da hukumar ta keyi, kana kuma ya musanta zargin da akeyi cewa ana amfani dasu don cin zarafin ‘yan adawa.

Kakakin yace” lalle muna nemansa ne game da binciken da jami’an mu keyi,kasa komai kakeyi sa an bashi wata manufa, ko ajiya mataimakinsa ya amsa gaiyatar da muka yi masa kuma yazo mun barshi ya tafi.”

Shi kuwa Ahmed Sajo kakakin Murtala Nyako, cewa yayi ba haka zancen yake ba inda an sarare abun da yafada da kunnen basira da ba haka ba.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:49 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG