Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kare Hakkin Bil-Adam Na Nijar Ta Samu Yabo


Hukumar Majalisar dinkin duniya mai kula da kare hakkin bil–Adam, ta jinjinawa hukumar kare hakkin bil-Adam ta kasar Nijar, a kasancewarta na kaiwa matakin sahun farko a jerin kasashen duniya dake fafutukar kare hakkin bil–Adam.

Wannan mataki da kungiyar ta samu zai bata damar yin jawabi a gaban majalisar dinkin duniya kamar yadda gwamnatin kasar Nijar zata iya yin jawabi a gaban hukumar kuma tana iya tsayawa takara a duk wani mukami a hukumance da ya shafi fafutukar hakkin bil-Adam.

Suma kungiyoyin dake kare hakkin bil-Adam, na jamhuriyar Nijar sun tabbatar da cewa rashin yin kasa a guiwa ne ya bata damar samun wanna matsayi kamar yadda daya daga cikin masu fafutuka akan kare hakkin bil-Adam, Malam, Jiboce Mago ya furta.

Yakar da cewa da wanna matsayi da hukumar ta samu wani nauyi ya sake hawa kanta na ganin cewa ta kara jajirce wajen kare hakkin bil-Adam, aninda yake dama shi take yi.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:33 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG