Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Zaben Ghana Zata Ilimantar Da Jama'a Kan Yadda Zabe Zai Kasance


Jami’an Hukumar zabe ta kasar Ghana na shirin ganawa da jagabannin jama’a da dattawa tare da shugabannin kafofin watsa labarai na kasar a cikin makon gobe don kaddamarda yakin wayar da kan jama’a dangane da babban zaben shugaban kasa da na ‘yanmajalisar dokokin da za’ayi ran 7 ga watan Disambar wannan shekarar.

Hukumar zaben tace zata tura jami’anta zuwa lungunan Ghana daban-daban don su ilmantarda mutane gameda yadda zaben zai gudana kuma su amsa tambayoyin jama’a.

A kwanan baya ne shugabar Hukumar zaben, Charlotte Osei, ta gana da manyan editocin kafafen watsa labarai don neman yin aiki da su don a tabattarda an gudanarda ingantaccen zabe kuma a cikin adalci.

XS
SM
MD
LG