Yakin da suka yi na ballewa daga kasar Pakistan don neman ‘yancin kai. Masu fafutukar da ke goyon bayan hukunta laifuffukan yakin Bangladesh, da kuma ‘yan uwan wadanda aka kashe a yakin sun goyi bayan wannan hukuncin kisa.
Wanda aka yankewa hukunci Motiur Rahman Nizami, wanda shine shugaban jam’iyyar musulunci mafi girma ta Jamaat-el-Islami. Wanda suka bayyana shi a matsayin wanda ya kitsa kisan malamai da wasu jama’a da fyade da azabtar al’umma a yakin.
Amma masu rajin kare ‘yancin bil’adama sunce, an rataye Nizami ne biyo bayan wata shari’a mai rauni a karkashin kotun hukunta laifuffukan yakin kasa da kasa ta kasar, inda ta yanke masa hukuncin kisa a shekarar 2014.
Tun dai shekarar 2010 shugaban dan shekaru 73 da haihuwa yake tsare a kurkuku, an kuma rataye shi da sanyin safiyar jiya Laraba, bayan kotun kolin kasar ta ki yarda da kokensa na hukuncin kisan tare da kin yarda ya nemi sassauci ga Shugaban kasar.