Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Idan Talakan Najeriya Bai Canja Ba, Kada Ya Tsammaci Canji Daga Shugabanni


Kauyen Yangalma, a kusa da Gusau, Jihar Zamfara a Najeriya
Kauyen Yangalma, a kusa da Gusau, Jihar Zamfara a Najeriya

Sai dai kuma wakilin Janar Buhari a wani taro a Lagos ya ce Najeriya tana bukatar shugaba ne mai hangen nesa, mai fada da cikawa da kuma nuna misali da kalamu da ayyukansa.

Gwamnatin Najeriya ta ce muddin 'yan kasar ba su taka rawar da ya kamata su taka ba, to kuwa zai yi wuya a iya samun ci gaban kasa mai ma'ana da kowa ke kwadayi.

Shugaba Goodluck Jonathan na Najeriya, shi ya fadi hakan ta bakin wakilinsa ministan ayyuka Mike Onelememen, a wani taron Cibiyar Samar Da Ayyukan Yi Ga 'Yan Najeriya a Lagos. Wannan shi ne karo na biyar da cibiyar take gudanar da irin wannan taron lacca a kan "Hanyoyin Inganta Mulki Mai Tasiri ga 'Yan Najeriya."

Shugaba Jonathan ya ce idan har dan Najeriya zai ki bin dokar kasa, to kuwa lallai yana yaudarar kansa ne idan har yana tsammanin kasa zata samu ci gaba.

Tsohon shugaban soja, Janar Abdulsalami Abubakar, da tsohon ministan ayyuka Dr. Hassan Lawal, wanda ya wakilci Janar Muhammadu Buhari a wurin wannan taron, duk sun yi magana kan abubuwan da suek ganin zai kawo ci gaban kasa.

Wakilinmu Ladan Ibrahim Ayawa, ya fara da tambayar Janar Abdulsalami Abubakar, ko yana ganin wannan taron zai yi wata fa'ida, ganin cewa ba yau aka saba gudanar da irin wadannann tarurruka ba, amma kuma har yanzu ba ta canja zani ba? Sai tsohon janar din ya kada baki yana cewa.

Janar Abdulsalam Abubakar Da Wakilin Janar Muhammadu Buhari A Taron Shugabanci Na Kwarai - 2:14
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:14 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG