Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ISIS Ta Yi Na'am da Mubaya'ar Boko Haram


Wasu mayakan kungiyar ISIS dauke da tutar kungiyar
Wasu mayakan kungiyar ISIS dauke da tutar kungiyar

Kasa da mako guda bayan da kungiyar Boko ta mika wuya ga kungiyar ISIS da ke kasashen Syria da Iraqi, kungiyar ta amince da mubaya'ar da ta samu, ta kuma ce hakan wata alama ce da ke nuna cewa ayyukanta na fadada zuwa sassan yammacin Afrika.

Kungiyar ISIS mai fafutukar kafa daular musulunci a kasashen Syria da Iraqi, ta amince da mubaya’ar da kungiyar Boko Haram ta yi ga kungiyar, wacce ke ta-da kayar baya a Najeriya.

A wani faifai da ISIS ta fitar a ranar Alhamis din da ta gabata, Kakakin kungiyar, Abu Mohammaed al-Adnani, ya yi maraba da wannan mubaya’a da kungiyar ta Boko Haram ta yi, ya na mai cewa hakan na nufin ayyukan kungiyar na kara fadada zuwa yankin Yammacin Afrika.

A cikin faifan, mai magana da yawun kungiyar ya ce Khalifa ya amince da wannan mubaya’a, ya na kuma taya abokanansu na Jihadi da ke Yammacin Afrika murna.

A makon da ya gabata ne shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau ya mika wuya ga kungiyar ta ISIS, inda ya ce a shirye su ke su bi duk umurnin da ISIS za ta ba su.

Babu dai masaniya game da irin yadda kungiyoyo biyu za su dinga hada kansu.

Ko a baya ma wasu kungiyoyin jihadi da ke sauran sassan duniya sun yi mubaya’a da kungiyar ta ISIS, ko da ya ke a lokuta da dama wasu na ganin hadin kan kungiyoyin na fatar-baki ne kawai da bai shige nuna wasu alamu kamar bayyana tutoci.

A wata hira da ya yi da VOA a farkon makon nan ne Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa ‘ya’yan kungiyar ta Boko Haram na samun horo daga kungiyar ta ISIS ne.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG