Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Litinin, Shugabannin Afirka Zasu Koma Abidjan Domin Tattaunawa Da Gbagbo


Tsohon ministan harkokin wajen Faransa yake tattaunawa da shugaba Laurent Gbagbo a fadar gwamnati a Abidjan.
Tsohon ministan harkokin wajen Faransa yake tattaunawa da shugaba Laurent Gbagbo a fadar gwamnati a Abidjan.

Shugabannin Afirka na ci gaba da daukan matakan Diflomasiyya domin warware matsalar siyasar zaben shugaban kasa dake addabar kasar Ivory Coast cikin lumana,

Shugabannin Afirka na ci gaba da daukan matakan diflomasiyya domin warware matsalar siyasar zaben shugaban kasa dake addabar kasar Ivory Coast cikin lumana, a dai dai lokacin da jami’an rundunar sojin kiyaye zaman lafiya na Majalisar dinkin Duniya ke cewa suna binciken ayyukan cin mutumcin Bil Adama da ake zargin ana tafkawa a Ivory Coast.

Friministan kasar Kenya Raila Odinga, zai hadu da sauran shugabannin kasashen Benin, da na Sierra Leone da Cape Verde, wani lokaci a yau litinin domin tattaunawa da shugaban dake kan gado na yanzu, Laurent Gbagbo.

Mr. Odinga, shine wakilin tarayyar Afirka dake shiga tsakani a rikicin siyasar Ivory Coast.

XS
SM
MD
LG