Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jakadiyar Faransa A Kamaru Ta Kaiwa Shugaban Majalisar Dattawa Ziyarar Bankwana


 Jakadiyar Faransa dake Christine Robbinson da Shugaban Majalisar Dattawan Kasar
Jakadiyar Faransa dake Christine Robbinson da Shugaban Majalisar Dattawan Kasar

Christine Robbinson jakadiyar kasar Faransa dake Kamaru ta kai ziyarar bankwana wa shugaban majalisar dattawan kasar ta Kamaru inda kuma ta samu ta yiwa 'yan jarida jawabi.

Jakadiyar tace ta kai masa ziyarar ce ta bankwana saboda ta kammala wa'adinta a kasarsa.

Tace ziyarar ta zamo wajibi domin sun yi aiki kafada da kafada da duk bangarorin gwamnatin ta Kamaru kama daga 'yan majalisu zuwa na zartaswa da shugaban kasa.

Tace zasu cigaba da taimakawa dakarun kasar Kamaru wajen ganin sun murkushe 'yan kungiyar Boko Haram da suke haddasa rigingimu a kasashe daban daban da suka hada da ita kanta Kamaru.

Dangane da dangantaka tsakanin majalisar dattawan Faransa da na Kamaru, Jakadiya Robbinson sai tace majalisar Faransa na bukatar kara habbaka dankon zumunci da na Kamaru.

Jakadiyar Faransa a Kamaru Christine Robbinson wadda ta kasance tamkar 'yar mulkin mallaka ce
Jakadiyar Faransa a Kamaru Christine Robbinson wadda ta kasance tamkar 'yar mulkin mallaka ce

Dr. Suleiman na ma'aikatar harkokin wajen Kamaru yace shi a nasa ganin bai ga wani aiki na musamman da jakadiyar tayi ba a kasar Kamaru musamman akan matsalar da suke fuskanta yau da kullum da 'yan Boko Haram. Kasar Faransa tayi alkawarin magance matasalar 'yan ta'addan amma har yanzu babu abun da suka yi. Yace har yanzu Fransa ta barsu akan mulkin mallaka duk da wai ta tafi amma har yanzu tana mulkinsu.

Ga rahoton Garba Awal da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:51 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG