Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jamhuriyar Nijar Na Zaman Makoki Na Kwana Uku


Shugaban Nijar Mahammadou Issoufou
Shugaban Nijar Mahammadou Issoufou

Gwamnatin Nijar ta kebe kwanaki uku na zaman makoki saboda sojojinta da kungiyar Boko Haram ta hallaka makon jiya a garin Bosso na jihar Diffa

Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta bada sanarwar kebe kwanaki 3 na zaman makoki daga yau Talata domin nuna juyayi akan mutuwar sojojinta da kungiyar Boko Haram ta hallaka a yayin kazamin harin da ta kai a ranar Juma’ar da ta gabata a garin Bosso dake jihar Diffa.

Sannan gwamnatin a karon farko ta bayyana adadin ‘yan ta’addan da sojojinta suka kashe a yayin wannan arangama a maimakon soja 32 da ta bayyana a can farko gwamnatin ta Nijar ta ce sojoji 26 ne kungiyar Boko Haram ta kashe yayinda sojojin suka kasha ‘yan kungiyar mayakan 55.

Ga karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:59 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG