Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jami'an Tsaro A Syria Sun Bude Wuta Kan Masu Zanga Zanga


Sojojin Syria suke sintiri.
Sojojin Syria suke sintiri.

Rahotanni na cewa akalla mutane tara ane suka halaka bayan da jami’an tsaron Syria suka bude wuta a kan masu zanga-zangar kin jinin Gwamnati.

Rahotanni na cewa akalla mutane tara ane suka halaka bayan da jami’an tsaron Syria suka bude wuta a kan masu zanga-zangar kin jinin Gwamnatin shugaba Bashar al-Assad na Syria a yau Juma’a.

Shaidun gani da ido suka ce jami’an tsaron Syria sun yi amfani da bindigogin dake dauke da harsasai suka rika harbin masu zanga-zangar a birnin Homs.

A halin da ake ciki, masu zanga-zangar sun ci gaba da gudanar da zanga-zangarsu a kan muhimman titunan biranen kasar Syria.

Kamfanin dillancin labarun Faransa ya jiwo daga bakin wani dan rajin Demokuradiya na cewa masu zanga-zangar suna rike da ganyen itatuwan Zaitun suna kirarin a basu ‘yancinsu.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG