Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam’iyar CPC Tana Shirin Fadawa Wani Sabon Rikici


Dan jam'iyyar CPC ne a nan ke rike da tutar jam'iyyar a lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa a Dandalin Mapo, dake birnin Ibadan.
Dan jam'iyyar CPC ne a nan ke rike da tutar jam'iyyar a lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa a Dandalin Mapo, dake birnin Ibadan.

An sami wani sabani tsakanin jam'iyar CPC ta jihar Kaduna da shugabannin jam'iyar na kasa kan batun jagorancin 'ya'yan jam'iyar.

Bisa ga dukan alamu tsuguni bata kare ba a yunkurin hada kan jam’iyun hamayya da nufin kwace iko daga hannun jam’iyar PDP mai mulki a Najeriya.

Wannan ya biyo bayan wani sabani da aka samu tsakanin ‘ya’yan jam’iyar CPC ta jihar Kaduna da shugabannin kungiyar na kasa yayinda hadakar jam’iyar hamayyar ta dauki matakan yin rajista a hukuma zabe.

Jam’iyar CPC a jihar Kaduna tayi zargin cewa, ta gano wadansu masu yunkurin yi mata zagon kasa a wannan hadakar.

Da yake jawabi ga manema labarai a jihar Kaduna, shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar Shehu Usman Adamu Danfulani, yace irin ikirarin da wadansu ke yi na zama shugabannin jam’iyar da ba a ma riga an yiwa rajista ba tukuna, ya sa kwamitin dattijan jam’iyar CPC ta jihar Kaduna, ya kafa wani kwamiti da nufin tsarkake jam’iyar daga dukan matsala.

Wakilinmu Isah Lawal Ikara ya aiko mana da hirarsu da bangarorin biyu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:28 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG