Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jana'izar Mutanen Da Aka Kashe A Madalla


Mata kenan ke kuka a yayin jana’izar bai daya ta wadanda su ka rasu a harin bam din ranar Kirsimeti a majami’ar Katolika ta St. Theresa.
Mata kenan ke kuka a yayin jana’izar bai daya ta wadanda su ka rasu a harin bam din ranar Kirsimeti a majami’ar Katolika ta St. Theresa.

An Yi Jana'izar Wadanda Harin Ranar Kirsimeti A Unguwar Madalla Ya Rutsa Da Su

Yau Laraba dubban mutanen da su ka hada da jami’an gwamnati da mambobin majami’u dabam-dabam ne su ka halarci jana’izar mutane 44, da harin bam din kunar bakin waken ranar Kirsimeti ya hallaka su a Majami’ar St. Theresa da ke unguwar Madalla da ke kusa da babban birnin tarayyar Nijeriya, Abuja.

Tuni dai kungiyar nan mai tsattsauran ra’ayin Islama ta Boko Haram, mai fafatukar kakaba tsarin shari’ar Musulunci a fadin Nijeriya ta dau alhakin kai harin.

Cikin wadanda suka halarci bison har da Limamin Kiristan Fadar Shugaban Niejriya wanda ya wakilci Shugaba Goodluck Jonathan na Nijeriya a wurin jana’izar.

Saurari:

Aika Sharhinka

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG