Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Janar Buhari Yace In Gwamnati Tana So, Za A Samu Zaman Lafiya


Janar Muhammadu Buhari mai ritaya
Janar Muhammadu Buhari mai ritaya

Jigon siyasar yace laifin gwamnatin tarayyar Najeriya ce irin rashin kwanciyar hankalin da ake ci gaba da gani a fadin Najeriya.

Jigon siyasa kuma tsohon shugaban soja na Najeriya, Janar Muhammadu Buhari, yace laifin gwamnatin tarayyar kasar ce irin tashe-tashen hankula da rashin tsaron dake wakana yanzu haka a fadin kasar.

A hirar da yayi da Muryar Amurka, Janar Buhari ya ce bai kamata gwamnati ta zauna kawai ta sanya idanu yayin da ake ci gaba da yin abubuwan da suke kokarin rushe kasar ba.

Janar Muhammadu Buhari Mai Ritaya Kan Batun Shirin Ahuwa Ga Boko Haram - 2:53
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:53 0:00
Shiga Kai Tsaye


Muhammadu Buhari yace shirin ahuwar da ake magana a kai a Najeriya zai yi aiki, amma sai idan an san su wanene a zahiri shugabannin kungiyar Boko Haram da ake son tattaunawa da su, kamar yadda aka yi na 'yan yankin Niger Delta.

Sannan kuma, ya sake nanata furucin da yayi tun farko cewa yanzu a Najeriya, akwai kungiyoyi uku dake kai hare-hare da sunan Boko Haram: watau kungiyar jama'ayu Ahlus Sunnati Lidda'awati Wal Jihad ta zahiri, da 'yan fashi dake fakewa da sunan wannan kungiya su na sata, da kuma 'yan ta'addar gwamnatin tarayya dake kashe mutane.
XS
SM
MD
LG