Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jihar Bauchi ta Bada Rahoton Cutar Kwalara Guda Uku


Mace dauke da danta mai fama da cutar kwalara
Mace dauke da danta mai fama da cutar kwalara

Ma’aikatar kiwon lafiya ta jihar Bauchi (PHCDA) ta sami mutane uku da suke sa zaton sun kamu da ciwon kwalara.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta jihar Bauchi (PHCDA) ta sami mutane uku da suke sa zaton sun kamu da ciwon kwalara.

Yayinda yake bayani ga manema labarai jiya, Sakataren wannan ma’aikata, Dr Nisser Ali Umar, yace: “An sami mutane uku a Kandahar yakin yan doya cikin Karamar hukumar Bauchi wadanda ake sa zaton sun kamu da ciwon kwalara ne. Mun sami labarin cewa almajirai biyu da kuma wani mutum daya a yankin suna fama da ciwon kwalara, nan take sai muka kwashe su muka kais u asibiti inda aka basu magani an kuma sallame su. An gane cewa babu ruwan sha mai tsabta a yankin, saboda haka mun sa magni a dukan rijiyoyin yankin. Haka kuma, ma’aikatar ruwa ta jihaar Bauchi ta shiga yankin domin gyara dukan pampunan da suka fashe.”

Ya kuma kara da cewa: “Yanzu, ba mu da damuwar cutar ta kwalera amma a shirye muke domin muna kewaye da jihohi masu wannan cutar. Wannan ma’aikata ta tanada magungunan, magungunan tsabtace wurare, da kuma safar hannu ga asibitocin da suke aiki a wadannan yankunan”.

Yayi kira ga shugabannin gargajiya da kuma na addinai a jihar da su taimaka wajen wayar da kan jama’a game da tsabtace muhallin su.

Melinda Gates

BIDIYO: COVID-19 VOA Ta Yi Hira Da Melinda Gates Kan Dalilin Da Yasa Suke Taimakawa Afirka
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:08 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG