Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ka Rike Amana Ko Ka Tafi Fursina - inji Janar Buhari


Janaral Muhammadu Buhari a Jihar Gombe, Fabrairu 3, 2015.
Janaral Muhammadu Buhari a Jihar Gombe, Fabrairu 3, 2015.

Janar Buhari yayi alkawarin gwamnatinsa zata shimfida adalci, idan har jama'a suka zabe su.

Dan takarar shugabancin Najeriya a inuwar jam'iyyar APC Janar Muhammadu Buhari mai ritaya, yayi alkawarin gwamnatinsa zata karfafa harkar ilmi ta wajen amfani da rarar kudi da zasu hana sataersu, wajen gina makarantu da samar da malamai.

Janar Buhari ya furta haka ne a lokacin da kwamitin yakin neman zabensa ya yada zango a jihar Gombe, jiha ta 34, ana saura kwanaki goma zuwa goma sha daya a fara zabe.

Janar Buhari yace babban abunda al'uma take bukata shine ilmi domin suyi dogaro dakansu.

Janar Buhari yace idan suka kafa gwamnati yana kashedin cewa, duk gwamnan da aka baiwa amanar jama'a sannan ya nuna kuriciyar bera, to yasan makomarsa.

Wakilin Sashen Hausa Abdulwahab Mohammed wanda ya zanta da 'yan jihar, sun bayyana irin goyon bayansu ga takarar Janar Muhammadu Buhari.

Ga rahoto.

Janar Buhari ya Gargadi 'Yan Takarar Gwamnoni a Inuwar APC - 3'27"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:27 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG