Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kananan Ma’aikata Sun Shiga Yajin Aiki A Nijar


Wadansu 'yan jamhuriyar Nihar suna jira su shiga mota a Kasuwar Katangua dake birnin Ikko
Wadansu 'yan jamhuriyar Nihar suna jira su shiga mota a Kasuwar Katangua dake birnin Ikko

Kananan Ma'aikata a Jamhuriyar Nijar sun shiga yajin aiki da nufin ganin gwamnati ta kyautata rayuwarsu.

Kananan ma’aikata sun shiga yajin aiki na kwana biyu a jamhuriyar Nijar da zumar tursasawa gwamnati ta biya bukatunsu ta hanyar sa hannu kan wani kundin da zai kyautata rayuwar ma’aikatan da suka haura dubu shida.

Ma’aikatan sun bayyana cewa, gwamnatin Jamhuriyar Nijar bata dauki kananan ma’aikata da muhimmanci ba, ta haka bata kulawa da wahala da kuma bukatunsu, suka kuma ci alwashin ci gaba da tursasawan gwamnati har sai sun sami biyan bukata.

Babban magatakardar hadakar kungiyar kananan ma’aikatan Kamarat Gagara Tasau ya bayyana cewa, kananan ma’aikata basu cin moriyar duk wani aikin da gwamnati ke yi na kyautata rayuwar ma’aikata da ya hada da gidaje da kuma taimakon jinyar likita idan su, ko iyalansu basu da lafiya.

Wakilinmu Abdoulaye Mamman Amadou ya bayyana cewa, ma’aitan sun shiga yajin aikin ne a daidai lokacin da majalisar ministoci take zama.
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:40 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG