Haka kuma ministan watsa labaran Gambia, Sheriff Bojang ya zargi kotun da nuna wariyar launin fata da kuma rashin yi wa kasashen Afrika adalci.
Yace koda yake ana kiran kotun “Kotun Kasa da kasa” kotun Turawa ce kawai da kullum take kuntatawa mutanen da ba Turawan ba, musamman mutanen Afrika.
Kusan dukkan shara’oi 10 da wannan kotun ta gudanar, in bayan guda daya tak, sun shafi kasashen Afrika ne.