Kakakin gwamnatin Janhuriyar Kamaru wanda shi ne kuma Ministan Sadarwar kasar, Isa Ciroma Bakari ya yi ma manema labarai jawabi a ofishinsa da ke birnin Yaoundé kan irin nasarorin da sojojin kasar ke samu a yaki da Boko Haram musamman a jahar Arewa Mai Nisa. Ya ce an fi fafatawar ce a wajejen kan iyakokin Najeriya da Chadi.
Ministan ya ce a ‘yan kwanakin nan sojojin Kamaru sun hallaka mayakan Boko Haram sama da 100, banda manyan makamai da motoci da kuma wayoyin salularsu da sauran kayan hada bama-bamai da su ka kwato. Ya ce su kuma ‘yan Boko Haram din sun kashe sojoji uku. Ministan ya ce ko a jiyan nan sai da wasu ‘yan mata ‘yan kunar bakin wake su hudu su ka tarwatsa kansu a wajejen kan iyakar Najeriya su ka raunata wasu ‘yan banga uku, wadanda aka garzaya da su asibiti.
Wakilinmu a Kamaru wanda ya aiko da rahoton, Awal Garba, ya yi hira da wani dan yankin Marwa mai suna Malam Abubakar kan yadda su ke ganin yanayin tsaro a yankin nasu sai ya ce gwamnatin Kamaru na ba da himma sosai wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin na Marwa.
Ga Muhammad Awwal Garba da cikakken rahoton: