Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Kamaru Na Nasara Kan Boko Haram


Shugaban Kamaru, Paul Biya.
Shugaban Kamaru, Paul Biya.

Bayan fatattakar 'yan Boko Haram da Najeriya ta ce ta yi daga dajin Sambisa, ita ma kasar Kamaru ta zayyana jerin nasarorin da ta ce ta yi a yaki da mayakan. Wannan na zuwa a daidai lokacin da Janhuriyar Nijar ma ke sassauta matakan tsaro a yankin Diffa saboda saukin da aka dan samu.

Kakakin gwamnatin Janhuriyar Kamaru wanda shi ne kuma Ministan Sadarwar kasar, Isa Ciroma Bakari ya yi ma manema labarai jawabi a ofishinsa da ke birnin Yaoundé kan irin nasarorin da sojojin kasar ke samu a yaki da Boko Haram musamman a jahar Arewa Mai Nisa. Ya ce an fi fafatawar ce a wajejen kan iyakokin Najeriya da Chadi.

Ministan ya ce a ‘yan kwanakin nan sojojin Kamaru sun hallaka mayakan Boko Haram sama da 100, banda manyan makamai da motoci da kuma wayoyin salularsu da sauran kayan hada bama-bamai da su ka kwato. Ya ce su kuma ‘yan Boko Haram din sun kashe sojoji uku. Ministan ya ce ko a jiyan nan sai da wasu ‘yan mata ‘yan kunar bakin wake su hudu su ka tarwatsa kansu a wajejen kan iyakar Najeriya su ka raunata wasu ‘yan banga uku, wadanda aka garzaya da su asibiti.

Wakilinmu a Kamaru wanda ya aiko da rahoton, Awal Garba, ya yi hira da wani dan yankin Marwa mai suna Malam Abubakar kan yadda su ke ganin yanayin tsaro a yankin nasu sai ya ce gwamnatin Kamaru na ba da himma sosai wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin na Marwa.

Ga Muhammad Awwal Garba da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:00 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG